Translate

Monday 13 January 2014

MAƊACIYAR ZUMA



 

MAƊACIYAR  ZUMA



“Aaah! Mutuwa? Asma’u me nake ji haka?”  Na  ƙwalla ƙara mai ƙarfin gaske daga banɗaki inda nake wanka tare da  jefar da littafin dake hannuna  ga ruwa na malala daga cikin bahon wanka a yayin da na yunƙura da ƙarfi dan  fita waje na tabbatar da abin da yake faruwa. Na garzayo da gudu a ɗimauce don zuwa falo, saura ƙiris na sha kwana kenan da zata sada ni da ɗakin sai naga hoton surar jikina tsirara lulluɓe da kumfa a jikin gilashin ƙofa, wanda hakan yasa na lura cewa ashe babu kaya a jikina. Sai na koma na ɗauraye kumfar dake jikina sannan na sanya kayana na fito.
          Ya zamar min al’ada duk safiyar lahadi, inda nake shiga bahon wanka wato (jacuzy)  don yin wanka. Tunda yake ƙarshen mako ne, sai nayi amfani da wannan damar inda nake karanta littafi  kafin na fita don halartar daurikan aure. Lahadi ta zamo ranar da aka fi yin ɗaure-ɗauren aure a garin Kano. Dan haka yasa ta zama tamkar ranar sakewa ga mutane da dama saboda damar da take basu na hutawa ba tare da  sun fita wajen harkokinsu ba tun sassafe kamar yadda aka saba.
          “Yanzinnan naji a rediyo,” Asma’u ta cigaba da faɗa min, “yanzu naji Nasir Zango yana faɗa a shirinsa na Inda Ranka.” Asmau ta kasance ma’abuciyar jin rediyo. Kullun safiya tana tashi ta kamo Muryar Amruka, BBC Hausa, DW ko RFI Hausa don ta ji labarai kafin daga bisani ta murɗo rediyo Freedom dan ta saurari shirin Inda Ranka  na karshen mako wanda jajirtaccan ɗan jaridar nan yake gabatarwa.
          “Kina nufin ya mutu?” Na tambayeta dan na samu tabbaci.
          “Ya mutu da gaske.” Asma’u ta tabbatar min.
          “To amma ya akai kika tabbatar shi ne?”
          “Kwatancensa da na ji an faɗa. Askinsa, kayansa da kuma yanayin fuskarsa.” Asma’u ta ci gaba da yi min jawabi, “iri ɗaya da kwatancen da muka bayar lokacin da muka kwana uku bamu ganshi ba.”

          Mun shiga wani zamani wanda akayi yayin zuwa ƙasashen waje, musamman ƙasar Malaysiya inda iyaye suke tura ƴaƴansu don yin karatu. Kowa ba shi da wani buri sama da yaga ya fitar da ɗansa ƙasar waje musamman idan yaro ko yarinya ya sami labaring tafiyar aboikinsa ko ƙawarta.  Suna tafiya da niyyar yin karautun kamar yadda suka sanar da iyayensu tun da fari. Amma da zarar sun je ƙasar sai su rikiɗa su zama kamar ‘yan yawon buɗe ido da shaƙatawa, sune kalle-kalle da halartar gidajen rawa, da gidajen shaye-shaye da sauran gidajen shagala. Kai a ƙarshe ma sune suke zama gawurtattun masu ta’ammali da sha da safarar miyagun ƙwayoyi wanda suke zama kamar wata annoba ga muhukuntar ƙasar. Amma saboda kuɗin shiga da suke samarwa da ƙasar, sai muhukunta sukayi shiru da bakinsu ba tare da ɗaukar wani mataki ba. Sai wanda da ya taɓa zuwa ƙasar ne kawai zai bada labarin haƙiƙanin miyagun ayyukan da yaran suke tafkawa a can.
          Ni dai na kasance mashahurin ɗan kasuwa mai zuwa ƙasashen duniya daban-daban don na sayo haja ko na sayar. A bisa haka ne zan bada wani labari  da ya faru a kaina. Wata rana ina balaguro zuwa ƙasar Dubai dan harkar kasuwanci na, sai na shiga jirgi tare da wani saurayi wanda ke kan hanyarsa ta komawa Malaysia inda yake karatu. Muka zauna a waje ɗaya a ɓangaren babbar kujera, wato dai sahun masu hannu da shuni wanda a turance ake kira da Fisrt Class.
          “Yaro kai ɗan Najeriyane?” Nayi wuf na tambayeshi cikin harshen turanci.
          “E,” shi ma ya amsa min.
          Na yi masa magana ne don mu ɗan yi taɗi tun bayan da na lura cewa duk munyi jugun-jugun kamar a gidan mutuwa. Nan ta ke na canja harshe zuwa harshen Hausa lokacin da na fahimci cewa shi ma saurayin bahaushe ne kamar ni. Ganin cewa ya sami ɗan uwa kuma abokin hira, sai yaron yaji daɗi sosai. Nan fa hirar mu tai nisa sosai kuma ta ɗau shauƙi inda nake tambayarsa shi kuma yana bani amsa. Saboda tsabar nishaɗin hirar har sai da na manta cewa a jirgi nake tafiya, na manta da doguwar tafiyar dake gabana, har ta kai sai da na manta da yinwar da nake ji kafin naci abincin da jami’an jirgin suka kawo min. Shi kansa abincin ban samu damar wai-wayarsa ba har sai da na samu wani ɗan taƙi inda hirar mu ta tsagaita. Yayin da na tambayeshi ko waye mahaifinsa, sai bayanan da na samu suka tabbatar min da cewa ya fito daga gidan wani Minista wanda ludayinsa ke kan dawo a gwamnati mai ci ta wannan lokacin. Ganin cewa a lokacin da yaje Najeriya ba lokacin hutu bane, sai na sa ke tambayarsa ko me yaje yi Najeriya. Nan ma sai ya sake gayamin cewa ya je ne don ya halarci bikin zagayowar ranar haihuwar ‘yar uwarsa (Birthday Party) wadda ita ma take karatu a ƙasar Amruka. Jin haka yasa na tuna da wani lokaci a baya wanda yawan ziyarar da ɗaliban najeriya masu karatu a waje ke kawowa gida yasa na tambayi Hajiya mahiafiyar Haladu, ɗan  yayana wanda tuni ya rigamu gidan gaskiya. Bisa yawan zirga-zirga da yake yi tsakanin Malaysia da Najeriya yasa na tambayi mahaifiyarsa cewa, “Hajiya shin wai  ina ne haƙiƙanin inda yaronnan yake karatune. A nan yake yi ne ko kuma a waje saboda ina ganinsa a gida kusan ko wace rana.” Na tambayeta cike da mamaki.
          Yayin da na tambayi abokin tafiyata, wato ‘yan samari, shin ko me suke yi idan suka zo Najeriya. Nan ma fa sai ya bani amsa da cewa ai suna zuwa shan fura ne kawai da kuma cin tsire a wani kantin sayarda kayan ƙwalam-da-maƙulashe da ke kan titin zuwa Zaria.
          “To amma ya kuke fama da zirga-zirga, kullun kuna kan hanya daga Malaysia zuwa Najeriya?” Na tambayeshi cike da mamaki da ta’ajibi.
          “Ya wancinmu anan iyayenmu ne suke saya mana jirgin yawo don biyan buƙatunmu ta yadda da munji kewar gida muna da damar mukai ziyara a kowane lokaci don mu sada zumunci ga ‘yan uwa da abokan arzuƙa.” Ya amsa cikin annashuwa da alfahari.
          “To amma ya akayi naga kuma ka hawo jirgin haya?”
Sai ya amsa da cewa, “ nawa jirgin ne ya lalace. Amma mahifina ya rigaya ya biyamin kuɗin tikiti da zan yi amfani da shi  har tsawon lokacin da zan gama karatuna.” Ya zira hannu a cikin jakarsa don ya fito min da takardun da za su gasgata abin da ya faɗa min. Ko da ya zaro takardun sai ga bandir ɗin Dalar Amruka ta faɗo daga cikin jakar wanda ganin haka yasa naji ba ni da wata buƙata ta ganin takardun.  Ganin irin fantamawar da yakeyi sai na tmbayeshi don ya gayamin ko wace makaranta yake zuwa a Malaysia. Sunan makarantar da ya faɗamin sai naji yayi dai-dai da sunan makarantar da ɗan yayana, Haladu yake halarta. Jin haka sai yasa na tambayeshi:
“Ko ka san Haladu?” wanda shi ne sunan ɗan yayan nawa da yake karatu a Malaysia. Ya ɗan rufe idanunsa kadan cikin tunani da rikici dan ya gano mutumin da nake kwatanta masa.
“Khalid Usman,” sai na ƙara masa haske dan ya gane wanda nake kwatanta masa cikin sauki. 
“Oho...” sai ya kece da dariya, “kana nufin Ɗan Hajiya ko? Ai idan ba kace Wizzy ba to ba zan taɓa ganewa ba.”
Bayan mun isa zuwa ƙasar Malaysia sai na ga ya dace na ɗan tsahirta a ƙasar  zuwa na ‘yan wasu kwanaki don na ɗan kewaya ko naga wata haja da zan iya siya kafin na wuce zuwa Dubai. Bayan  mun fito daga ɗakin bincike, sai nayi masa tayi ko zai kwana a masauki na kafin safiya, amma sai yace a’a. Daga nan sai mukayi musayar adireshi inda yayi alkawarin cewa zai zo ya ɗaukene washegari daga masauki na don nakai ziyara makarantarsu. Mukai sallama na shiga motar haya don zuwa masauki inda na bar yaron tare da jerin gwanon motoci da suka zo su tarbeshi.
Washegari saurayinnan yazo ya ɗaukeni izuwa makarantar. Lokacin da na shiga na zata ko ina Najeriyane sakamakon yawan ‘yan Najeriya da nayi ido huɗu da su. Dukkanninsu suna cikin farin ciki da jin daɗi kuma kowa yana yin abin da ya ga dama dan babu mai kwaɓarsu. Babu mai cewa ta tafasa balle ka sauke. Abin dai ba kyan gani yadda suke cakuɗe-ɗeniya tsakanin maza da mata har ta kai da ba’a iya ban-bancewa tsakanin jinsi. Suna ta cashewa abinsu, ga kiɗa na tashi ta ko’ina daga cikin motocin dake ajiye a wurin. Kayan maye a wurin sun zama kamar ruwan sha kowa sai kwankwaɗa yake. Wasu na tayiwa kansu allurai, wasu kuma nata busa hayaƙin taba sama, yayinda wasu ke shaƙa hodar iblis cikin hancinsu.  Ina tsaye sai ga wasu yara mace da namiji sunzo wucewa suna tafiya suna tunɓele da karafkiya suna haɗa hanya kamar ‘ƴa’ƴan agwagwa. Na kiɗima ƙwarai da gaske yadda naga yarinyar tana haɗiyar ƙwayoyi tana binsu da ruwan magani, (syrup). Ganin yadda aka san matan Hausawa da tarbiya, sai na yunƙura don naje wajen yarinyar nayi mata magana nace ‘ƴan mata ko ke ba bahaushiya bace,’  sai kawai naji tayi magana da yaran kuma a cikin kammalalliyar Hausa kamar jakar Kano. Bayan sun matso kusa da inda nake tsaye sai naga ashe Salima ce ‘ƴar abokina wanda ya taɓa yin gwamna a maƙwabciyar jahar mu. Shi kuma yaron da ke tare da ita ko da na tambaya ko shi waye sai aka gaya min cewa ɗa ne ga wani babban Jami’in gwamnati daga Jahar Enugu wanda ya taɓa rike muƙamin Ministan Man Fetur a gwamnatin da ta shuɗe.
Ɗan Hajiya da abokansa suna ɗaki bayan sun gama buguwa da kayan maye, suna tattauna yadda zasu halarci wani casu da za’ayi daddare.
          “Wizzy wai ya za’ayine kasan fa akwai casu yau da daddare?” Abokin Ɗan Hajiya mai suna Zicko ya tambayi abokinsa. Asalin sunansa shi ne Adamu amma ganin cewa sunan yayi masa nauyi sai ya canja zuwa Zicko don ya tafi da yanayinsa.
“Ai yau akwai wani babban casu, duk wani yaro mai ji da kansa a ƙasar nan zai je.” Khalid Ɗan Hajiya ya faɗa.
“Dole ne fa mu cinye kowa a wajen casunnan kai ka sani abokina.” Ɗayan abokin nasu mai suna Bross shi ma ya tofa albarkacin bakinsa. Yana magana ga kuma naɗin tabar wiy-wiy a hannunsa yana ta faman zuƙa yana busa hayaƙin sama ta hanci da baki kamar  tsohuwar motar da salansarta ta fashe. “Akwai ragowar ƙwayoyi kuwa? Kun san fa da ita ne zamu iya wuce sa’a a ko’ina. Yawan ƙwayar da muka sha shi zai sa mu burge kowa da kowa a wajen.”
“Ka gama har wasu ma bawa waɗanda basu da ita da yawa.” Zicko ya jaddada abinda abokinsa Bross ya faɗa.
“Duk  ƙwayoyinnan fa sun ƙare. Na shanyesu duka yau da safannan kuma kun san kwanannan kuɗi wahala suke.” Ɗan Hajiya ya maida musu da amsa.
“Haba mutumina, meye amfanin Hajiya idan ba zata baka kuɗi ba? Kawai ka gaya mata baka da kuɗi za ta sa wannan ƙanin babannan naka ya ba ka.”        
Tsaowon lokaci ke nan bayan dawowata daga ƙasar Malysia inda naga irin mashaa da yaranmu ke tafkawa da sunan karatu. Wata rana Ɗan Hajiya ya dawo gida ya gayawa mahiafitayrsa ƙaryar cewa anyi hutun makaranta kamar yadda ya saba duk lokacin da yake so ya zauna a gida. Ina zaune a gida tare da matata Asmau ina gaya mata abinda yake damuna an halayyar Ɗan Hajiya.
Wannan sha-shan yaron, na kama faɗa cikin fushi. ya ƙi ya nutsu ya san abinda yake ciki. Yaƙi ya maida kai akan karatunsa gashi kuma kasuwarma yaƙi ya fuskanci abinda ake koya masa. Ni dai ban san yaushe zaiyi hankaliba.
Alhaji, Asmau ta fara bani haƙuri, kayi haƙuri kasan yaran yanzu sai da haƙuri da kuma addua. Kullun ina gaya maka ka daina sa kanka cikin damuwa idan kuma ba haka ba sai hawan jini ya kamaka.
Amma dai ai baa zuba ido ba a bar abubuwa su ringa faruwa sasakai ba. Matasannan fa sune manyan gobe kuma a wannan lokacin ne ya kamata su ginawa kansu makoma me kyau. Amma ki duba ki gani ba abinda suke shagala da shi sai shaye-shaye, sata da zuwa gidan rawa. Yanzu kinga ma fa ya sayarda motar da Hajiya ta saya masa yayi mata ƙaryar cewa wai an sace.
Bayan na gama banbaimi na ban zame ko ina ba sai gidan Hajiya don na gaya mata abinda yake faruwa. Duk da yake ƙarfe 3:00 na yamma ta riga ta yi lokacin da  na iske gidan, amma har kawo wannan lokacin Ɗan Hajiya bai tashi daga barci ba saboda kayen mayen da yasha daren jiya.
Hajiya na gaya miki kina shagwaɓa yarannan. Abin yayi yawa Hajiya, ace yarannan ya zama kamar ma shi ne babar taki sai abnida yace shi kike yi. Yanzu ga shi yazo ya share waje ya zauna sama da wata uku kuma yana gaya miki cewa wai anyi musu hutune. Su makarantar basu da hankaline.Ina ta faɗa cikin fushi ina girgiza kaina cikin nadamar Ɗan Hajiya.
Nan fa Hajiya ta hayayyaƙo ƙaina tana ta balbaleni da masifa tana cewa, me yasa zaka takurawa ɗa na iye? Ka ƙyale shi ya sakata ya wala.
Amma Haji...
Amma me? Hajiya ta katseni kafin na ƙarasa. Da ma ina so na gayama cewa wai baka san kayi min laifi ba da ka koroshi daga kasuwa kuma shi ne yanzuma har kake iya buɗe baki kana gayamin wannan maganar. To gaya min mai yayi ka koroshi, iye? Hajiya ta tambayeni cikin fushi tare da tsare ni da ido tsuru-tsuru, ta tsaya a gabana tana gallamin harara kamar ta cukumeni da kokawa.
Na kama shi yana ɗibar kuɗi shi yasa na kore shi. Kuma da ma na gaya masa kada ya sake na ƙara kamashi yana yin sata.
Amma ka san cewa kuɗin ba naka bane kai kaɗai ko? Ta faɗa a cikin gatse. To shi ma yana da gado.
Amma dai Hajiya a matsayina na ɗan uwan mahifinsa bai kamata ina gani ba yarannan ya lalace. Ai alumma sai su tsine min suce ban sauke haƙƙin da ya rataya a wuyanaba. Na cigaba da yi mata jawabi laalla ta fahimce ni.
Bayan tafiyata a wannan rana, ashe Ɗan Hajiya da abokansa suna da casu da daddare wanda suke kira shakwaro (shokorology). Ɗan hajiya yaje wajen mahifiyarsa ya gaya mata ƙarya da gaskiya kamar yadda ya saba duk lokacin da yake buƙatar wani abu a hannunta. Ita kuwa sai ta ba shi kuɗi wanda da su ne yake biyan buƙatunsa na siyan kayan maye. Bayan da dare yayi Ɗan Hajiya da abokansa suka yi shiga irin wadda suka saba yi, tsukakken wando da matsatstsiyar riga ga ɗamara wato belt a waje ga rabin ɗuwawunsu shi ma duk a waje ana gani, wato sukayi shiga irin ta samfurin suwaga. Ba iya nan suka tsayaba, kai hatta askin kansu ma irin samfurin nanne mai taken Bollatalli. Bayan sun sha ƙwaya tun a gida ta fara yi musu karo sai suka fita abinsu zuwa wajen casu suna ta tunɓele a hanya. Duk wanda ya gansu sai ya kauce ya basu waje dan gudun kada su jefashi cikin lambatu saboda karafniya da suke suna haɗa hanya. Da zuwa wajen casun, sai dukkaninsu saku zube ƙasa cikin maye saboda basa cikin hayyacin da zasu iya zama ballantana su tsaya su kalli ma me yake gudana. Gida ya cika da samari maza da mata ana ta tiƙar rawa.
Can daga tsallaken inda suke rawa wani mutum ya garzaya zuwa ofishin yan sanda dan bada rahoton ɓatar motarsa da aka sace  bayan da ya shiga wani kanti dan yayi siyayya akan hanyarsa ta komawa gida daga wajen aiki. Ya shiga ofishin ƴan sanda a ɗimauce yana kuka wi-wi hannuwa a ka. Babban jamiin ƴan sanda wato DPO ya tura mutanensa dan su bi sawun ɓararyin.  Amma sakamakon cewa ɓarayin basu da wata tartibiyar siffa da zaa iya ganesu, sai DPO yace de yaransa su kamo duk wanda suke ganin yayi shige da masu aikata laifi idan yaso a gane mai laifi da maras laifi daga baya bayan anyi bincike. Ƴan sanda na fita basu zame ko ina ba sai inda ake casu da shaye-shaye wajen da nanne masu laifi su kan samu mafaka. Da isarsu sai  kowa ya gudu abinsa, wasu suka haure ta katanga, wasu kuma suka zillewa ƴan sandan, kai wasu ma sai da akai kokawa da su aka kai ruwa rana sannan suka samu suka kufce da ƙyar, irin abinnan da Huasawa suke cewa wai da ƙyar na sha... Amma su kam su gogannaka basu ma san me ake cikiba domin kuwa a sailin ne ma ƙwaya ta fara aiki gadan-gadan. Suna nan kwance sun kasa ko motsawa balle su gudu inda suke ta barci sharkaf kamar kasa.
Waɗannan ne ɓarayin." Ɗaya daga cikin jamian tsaron ya faɗi haka. Sajen kalle su fa, kalli kayansu, kalli askinsu, kalli fuskarsu da idanunsu, ai kawai yallaɓai su ne ma. Nan ta ke ƴan sanda sukayi awan gaba da su zuwa chaji ofis dan gudanar da bincike inda nanne Ɗan Hajiya ya mace sakamakon ciwon kansar hunhu da ya tayar masa ba tare da ya sha magani ba bayan kwana uku muna ta faman nemansa. Ta haka ne mukayi ta nemansa kafin mu ji labarin balin da ya same shi a rediyo. A washegarine mukaje don ɗauko ragowar gawarsa a ofishin ƴan sanda inda gawar har ta fara ɗoyi saanna muka binne shi. Da fatan Allah ya jiƙansa!  

No comments:

Post a Comment